EDITA.
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa zai goyi bayan duk wanda jam’iyyar ADC ta zaɓa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Atiku, wanda shi ma ke neman takarar a ƙarƙashin jam’iyyar, ya jaddada cewa haɗin kai da mutunta zaɓin jam’iyya su ne ginshiƙan nasara, yana mai nuna aniyar sa ta aiki tare da duk wanda ya samu tikitin takara.










