RIVERS: Majalisa ta ja kunnen shugaban riko …

HASSAN TURAKI.

Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbas Tajudeen, ya tunatar da shugaban rikon kwarya na Jihar Ribas, Bice Adimiral Ibok-Ete Ekwe Ibas, kan iya hurumin da yake da shi na shugabancin wannan rikon kwarya, karkashin dokar ta-baci a halin yanzu.

Shugaban majalisar, ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da wani kwamitin wucin-gadi mai dauke da wakilai 21, wanda aka dora wa alhakin sa ido kan harkokin mulki a jihar, inda aka dakatar da tsarin demokuradiyya, sakamakon ayyana dokar ta-baci da shugaban kasa ya yi.

Yayin da yake bayyana makasudin kafa kwamitin, Kakakin Majalisar Abbas ya bayyana cewa, aikinsa zai kasance a matsayin, “Sa ido kan yadda ake aiwatar da umarni da kuma tsare-tsaren gwamnatin tarayya a jihar ta Ribas, tabbatar da cewa; gwamnatin rikon kwarya tana bin doka da kare muradun jama’a tare kuma da samar da damar sake kafa cikakken mulkin demokuradiyya.

Ya jaddada cewa, dole ne ayyukan shugaban rikon kwaryar su yi daidai da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasar, tare kuma da tabbatar da aiwatar da gaskiya da rikon amana.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *