ASHIRU GAMBO.
Mai Girma Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya kafa wani kwamitin musamman domin sa ido da kuma jagorantar rabon gidaje 1,000 da aka gina a Malkohi, bisa kudurinsa na tallafa wa al’ummar jihar da gidaje masu araha.
Kwamitin yana karkashin jagorancin Hon. (Dr) Abdullahi Adamu Prambe, Kwamishinan Harkokin Gidaje da Cigaban Birane. Mambobin kwamitin sun hada da:
Wakilai daga Gwamnatin Jihar Adamawa
Akanta Janar na Jihar
Kwamishinan Shari’a
Shugaban Ma’aikatan Nesa da Nesa (Surveyor General)
Babban Sakataren Ma’aikatar Gidaje
Babban Sakataren Sashen Siyasa
Mataimakin Babban Sakataren Ma’aikatar Gidaje
Sauran wakilai a cikin kwamitin sun hada da:
Wakilin Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC)
Wakilin Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (SSS)
Wakilin Bankin Lamuni na Gidaje na Jihar Adamawa
Babban burin wannan kwamiti shi ne tabbatar da gaskiya, adalci da kuma bayyana gaskiya a cikin rabon wadannan gidaje, domin tabbatar da cewa al’ummar jihar Adamawa sun amfana da manufofin Gwamna Fintiri na samar da gidaje masu saukin samu kamar yadda kwamitin ya tabbatar.
Leave a Reply