LND: A duba maganar Sanata Natasha …

Hassan Turaki.

Zargin da ake wa Sanata Akpabio zargi ne mai nauyi da ka iya taba martabar Majalisar Dokokin Nijeriya kai tsaye hakan zai iya zubar da mutuncin kasar a idon duniya

Dan haka wajibi ne a gudanar da sahihin bincike don gano hakikanin abin da ya faru tsakanin Sanata Natasha da Akpabio in ji mai magana da yawun kungiyar habbaka dimokradiyyar arewacin Najeriya, Dr. Ladan Salihu.

Ladan ya cigaba da cewa babu hujja irin wannan matsaloli suna faruwa kuma ana ji ana gani ayi shiru, ya zama wajibi ayi duba na tsanaki kasancewar majalissar dattawa Najeriya itace martabar kasar a ciki da wajen Najeriya.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *