Education

Yar shekara 17 daga yobe ta lashe gasar turanci na duniya

Hassan Turaki.

Matashiya ‘Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya Da Aka Gudanar A Birnin Landan

Nafisa Abdullah Aminu, yarinya ‘yar shekaru 17 daga jihar Yobe, ta samu babban nasara a gasar ƙasa da ƙasa ta harshen Turanci da aka gudanar a London, Birtaniya, ƙarƙashin TeenEagle Global Finals 2025.

Nafisa, wadda ke karatu a Nigerian Tulip International College (NTIC), Yobe, ta fice daga cikin fiye da ɗalibai 20,000 daga ƙasashe 69 – ciki har da waɗanda harshen Turanci ke matsayin na uwa-uba a wurinsu.

Wannan gagarumar nasara da ta samu ana kallonta a matsayin abin alfahari ga Najeriya da nahiyar Afrika gaba ɗaya, duba da asalin jihar da ta fito wadda ke fama da ƙalubale a harkar ilimi da tsaro.

A sakamakon haka, hukumomi da malamai a jihar Yobe sun nuna farin ciki da wannan nasara, suna fatan za ta zama abin ƙarfafa guiwa ga sauran matasa domin yin fice ta hanyar ilimi da ƙoƙari.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button