Politics

NNPP NIGERIA: Jam’iyyar nnpp ta magantu kan takarar kwankwaso

Hassan Turaki.

Jam’iyyar NNPP, ta bayyana cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi mata takarar shugaban ƙasa a 2023, ba zai tsaya takara a 2027 ba.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dokta Agbo Major, ne ya bayyana haka a wata sanarwa, inda ya mayar da martani kan wata magana da Buba Galadima ya yi.

Galadima, ya ce har yanzu Kwankwaso yana cikin NNPP kuma zai tsaya takara a 2027.

Galadima ya shaida wa manema labarai cewa: “Babu wani tabbaci da ke nuna cewa Kwankwaso yana shirin komawa APC. Za mu ci gaba da zama a NNPP har lokacin zaɓen 2027 ya zo. Muna kira ga ’yan Najeriya su mara masa baya.”

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button