Politics

2027: Jam’iyyar ADC ce zata kara da APC

EDITA.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya ce goyon bayan da wasu gwamnonin APC suka nuna wa Shugaba Bola Tinubu domin ya sake tsayawa takara a 2027 bai dame su ba.

Ya ce su a cikin ƙungiyarsu ta masu haɗaka sun fi mayar da hankali ne kan talakawa, ba shugabanni ba.

Ƙungiyar masu haɗaka ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar, Peter Obi, da Nasir El-Rufai ta zaɓi jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar da za su kara da APC a zaɓen 2027.

“Mun ƙudiri niyya sosai. Muna da ƙwarewa kuma muna aiki a hankali. A lokacin da ya dace ne za mu bayyana wa duniya shirinmu,” in ji shi.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button